No Result
View All Result
  • Login
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Kasashen Ketare
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
CONTACT US
SUBSCRIBE
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Kasashen Ketare
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
No Result
View All Result
Home Labarai

Asibitin Usman Danfodiyo ya dakatar da ma’aikaciyar da ta caccaka wa jaririya allura

Yan kwanaki kenan bayan bazuwar labarin wata ma'aikaciyar jinya da ta caccaka allura wa wata jaririya a asibitin koyarwa na Usman Danfodiyo dake Sokoto, asibitin ya bada umarnin dakatar da ita nan take.

Bashir Khalid Furyam by Bashir Khalid Furyam
July 17, 2021
in Labarai
Reading Time: 2 mins read
4 0
0
Asibitin Usman Danfodiyo ya dakatar da ma’aikaciyar da ta caccaka wa jaririya allura

Yan kwanaki kenan bayan bazuwar labarin wata ma’aikaciyar jinya da ta caccaka allura wa wata jaririya a asibitin koyarwa na Usman Danfodiyo dake Sokoto, asibitin ya bada umarnin dakatar da ita nan take.

RELATED POSTS

Na Yi Kuskure A Zaben Mataimakin Shugaban Kasa A 1999– Obasanjo

Na Yi Kuskure A Zaben Mataimakin Shugaban Kasa A 1999– Obasanjo

June 26, 2022
Shugaban INEC Mahmood Yakubu

Zaɓen Osun, sai yafi na Ekiti Inganci — Alwashin Shugaban INEC ga Masu Kaɗa ƙuri’a

June 26, 2022
Zan taya murna ga Kowacce Jam’iyya taci zaɓen Shugaban Ƙasa a 2023 — Hadimar Buhari

Hadimar Buhari Onochie, ta musanta batun cewa Tinubu bai da Takardun makaranta

June 26, 2022
Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari

Cikar Shekaru 60: Ka cigaba da yiwa Najeriya aiki – Buhari ga Gbajabiamila

June 26, 2022
Gwamnan Zamfara Bello Matawalle

Matawalle ya umarci Mazauna Zamfara dasu ɗauki Makamai su kare kansu akan ƴan bindiga

June 26, 2022
Mutane 6 Sun Mutu, 4 Sun Sami Rauni A Hadarin Mota A Jihar Jigawa–FRSC

Mutane 6 Sun Mutu, 4 Sun Sami Rauni A Hadarin Mota A Jihar Jigawa–FRSC

June 25, 2022

Ma’aikaciyar jinyar ta ce ta yi wannan mummunar aika-aika ne da zummar ramuwar gayya kan abinda mahaifiyar jaririyar ta yi mata na maido da ita makaranta sakamakon kada ita a jarabawa wato Carry Over a turance.

Da yake jawabi wa manema labarai a birnin Sakkwaton Shehu, Babban Daraktan Lafiya na asibitin mai suna Dakta Anas Sabir ya ce ma’aikaciyar jinya da a yanzu haka take tsare a gidan gyaran tarbiya dake jihar, ya ce dakatarwar tata zai ci gaba ne har sai abinda bincike ya tabbatar.

Ya ce “Idan aka kama ta da laifi yo tilas ne mu kore ta daga aiki baki ɗaya, amma yanzu dakatarwar har sai baba ta gani ne”

Idan ba a mance ba dai makonni biyu da suka gabata ne aka zargi ma’aikaciyar da caccaka wa jaririyar allura jim kadan bayan zuwanta duniya wai da zummar daukar fansar abinda mahaifiyarta ta yi mata a Cibiyar Jami’ar Karatu daga gida inda nan ne mahaifiyar tata ke aiki.

Da take zantawa da manema labarai, mahaifiyar jaririyar mai suna Asma’u Ahmad Tijjani ta yi waiwaye cewa nas din ta sameta ana makonni biyu gabannin haihuwarta kan cewa tana da wani sirri da ita da take son tattaunawa.

Ta ce “Bayan na tashi kan mu yi magana, sai ta fara mun tambayoyi, shin yaushe ne ake sa ran zan sauka, sannan yaushe zan je asibiti kuma menene cikakken sunana?

Buy JNews
ADVERTISEMENT

“To ganin cewa babu wata alaƙa ta keke da keke da ta taba hadani da ita, ya sa na ƙi gaya mata duk wadannan abubuwa da ta tambaya” Cewar Asma’u.

To sai dai a cewar mahaifiyar jaririyar, ma’aikaciyar jinyar mai suna Folake Folasade ta nusar da ita kan cewa tana da muradin taimaka mata ne yayin hajihuwar tata, lamarin da ya sa ta saki jiki.

“Jim kadan bayan na sauka lafiya ne sai ta zo ta karbi jaririyar don nuna ta wa mai gidana, ganin cewa ban aminta da ita ba sai na ce wa wasu nas-nas da su bi ta amma ta yi kirmimis ta ce ba za a yi haka ba”

Ta kara da cewa “Bayan wasu yan mintoci sai gata ta dawo mun da jaririyar, dauke da jini shame-shame a fuskarta, hakan ya sa ni tusa ihu amma kafin a ankara a nemeta an rasa”

Yanzu haka dai an sallami wannan mahaifiya da jaririyar ta daga asibiti, amma abinda ya fi ɗaga wa likitoci da ita kanta Asma’u shine tabbacin ko shin jaririyar za ta iya gani ko a’a, lamarin da aka ce sai ta fara girma za a tabbatar da hakan.

Tags: Usman Danfodiyo
Share2Tweet2Share1
Bashir Khalid Furyam

Bashir Khalid Furyam

Related Posts

Na Yi Kuskure A Zaben Mataimakin Shugaban Kasa A 1999– Obasanjo
Labarai

Na Yi Kuskure A Zaben Mataimakin Shugaban Kasa A 1999– Obasanjo

June 26, 2022
Shugaban INEC Mahmood Yakubu
Siyasa

Zaɓen Osun, sai yafi na Ekiti Inganci — Alwashin Shugaban INEC ga Masu Kaɗa ƙuri’a

June 26, 2022
Zan taya murna ga Kowacce Jam’iyya taci zaɓen Shugaban Ƙasa a 2023 — Hadimar Buhari
Siyasa

Hadimar Buhari Onochie, ta musanta batun cewa Tinubu bai da Takardun makaranta

June 26, 2022
Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari
Labarai

Cikar Shekaru 60: Ka cigaba da yiwa Najeriya aiki – Buhari ga Gbajabiamila

June 26, 2022
Gwamnan Zamfara Bello Matawalle
Tsaro

Matawalle ya umarci Mazauna Zamfara dasu ɗauki Makamai su kare kansu akan ƴan bindiga

June 26, 2022
Mutane 6 Sun Mutu, 4 Sun Sami Rauni A Hadarin Mota A Jihar Jigawa–FRSC
Labarai

Mutane 6 Sun Mutu, 4 Sun Sami Rauni A Hadarin Mota A Jihar Jigawa–FRSC

June 25, 2022
Next Post
Manyan Antoni Janar na Kudu maso yamma sun yi ganawar sirri a Ekiti

Manyan Antoni Janar na Kudu maso yamma sun yi ganawar sirri a Ekiti

FG ta amince da biliyan 6.25 don kiwon shanu a Jahar Katsina

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Siyasa

  • All
  • Siyasa

YANZU-YANZU: Dino Melaye Ya Sake Shan ‘Kasa A Kotun Daukaka Kara

October 11, 2019

An kai Rundunar sojin sama Kudancin Kaduna domin kawo ƙarshen matsalar tsaro

August 16, 2020
Zamu binciko wadanda suka kashe Ibn Na-Allah, inji Rundunar Yan sanda

Yan bindiga sun hallaka Yan Sakai biyu a Niger

September 7, 2021

Facebook

Twitter

Labarai

  • Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    25 shares
    Share 10 Tweet 6
  • Yan sanda a Katsina sun cafke yaro dan shekara 13 saboda ya kashe yan ta’adda

    15 shares
    Share 6 Tweet 4
  • Abuja: Musa Ɗan Shekara 16 shiya koya man neman Maza — Cewar Matashi Mai shekaru 36

    692 shares
    Share 277 Tweet 173
  • Yadda na rinka lalata da yar shekaru 32, cewar dan shekaru 13

    40 shares
    Share 16 Tweet 10
  • Asibitin Usman Danfodiyo ya dakatar da ma’aikaciyar da ta caccaka wa jaririya allura

    6 shares
    Share 2 Tweet 2
Dimokuradiyya

An Kafa Jaridar Dimokuradiyya Ne Domin Tabbatar da mulkin da Jama'a suka zaɓa da Kansu Domin su Amfana.

Recent Posts

  • Na Yi Kuskure A Zaben Mataimakin Shugaban Kasa A 1999– Obasanjo
  • Zaɓen Osun, sai yafi na Ekiti Inganci — Alwashin Shugaban INEC ga Masu Kaɗa ƙuri’a
  • Hadimar Buhari Onochie, ta musanta batun cewa Tinubu bai da Takardun makaranta

Quick Links

  • Tsaro
  • Siyasa
  • Labarai
  • Wasanni
  • Kasuwanci
  • Rikicin Duniya

Contact Us

info@dimokuradiyya.com.ng

0809 912 4425 +234 809 912 4425

No. 218 Mogadishu layout Kaduna City Center Ahmadu Bello way kaduna. Kaduna, Nigeria 800273

© 2021 Dimokuradiyya Media Services LTD - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Kasashen Ketare
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • Kiwon Lafiya
  • Ilimi
  • Kasuwanci
  • Noma Da Kiwo
  • Talla
  • Masarautu
  • Babu Maraya
  • Addini
  • Wa’azin Kirista
  • Girke-Girke
  • Waiwaye
  • Marubutanmu
  • Wasiku
  • Ni’ima Dai Mata
  • Bidiyo
  • Hotuna
  • Mujalla
  • Shirye-Shirye Na Musamman
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Yan Fim da Finafinai
  • Zauren Dimokuradiyya

© 2021 Dimokuradiyya Media Services LTD - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In