Jaridar Punch ta rawaito cewa gwamnan jihar Abia Governor Okezie Ikpeazu ya kamu da cutar sarke numfashi.
Hakan ya fito daga bakin kwamishinan yada labarai na jihar John Kalu, a yau Litinin.
Kwamishinan yace gwamnan ya killace kansa kamar cibiyar dakile cututtuka ta kasa ta kafa doka.
Yace “idan ba a manta ba ranar ga watan da ya gabata ne mai girma gwamna ya dauki gwajin cutar, kuka cikin nasara gwajin ya tabbatar yana yana da cutar”.
https://dimokuradiyya.com.ng/covid19-gwamn-ikpeazu-ya-killace-kansa-sakamakon-rasuwar-kwamishinansa/
“Mai girma gwamna ya sake daukar gwajin a karo na biyu domin tabbatar da sakamakon, kuma sakamakon ya sake tabbatarwa yana dauke da cutar”.
“Sakamakon haka yasa gwamna Okezie Ikpeazu ya killace kansa don bi dokar da NCDC ta kafa wajen ganin an dakile cutar”.
Kalu ya kara da cewa gwamnan ya umarci mataimakinsa Ude Chukwu da ya ci gaba da gudanar da harkar shugabanci a jihar kafin ya warke.