Kocin Arsenal, Mikel Arteta ya yi tunani kan karshen zawarcinsu na gasar Premier ranar Asabar,Daily Post ta rawaito.
Rashin nasarar da Gunners suka yi a Nottingham Forest da ci 1-0 na nufin Manchester City ta zama zakara kafin wasansu da Chelsea ranar Lahadi.
KARANTA WANNAN LABARIN: UCL: Abin Da Guardiola Ya Gaya Mani Kafin Wasan City da Madrid – Rio Ferdinand
Arteta ya yarda cewa ya shiga “mawuyacin lokaci a cikin makonnin da suka gabata” yayin da suka ruguje yayin fafatawar.
“Mun samu sauyi sosai a wannan kulob din, mun yi manyan matakai, amma abin da ake so a kai shi ne lashe gasar zakarun Turai kuma mun gaza.
“An sha wahala a ‘yan makonnin da suka gabata. Muna buƙatar ƙungiyar tare da kowa a cikin mafi kyawun su a cikin Afrilu da Mayu, kuma hakan bai faru ba.
Arteta ya shaida wa BBC MOTD cewa “Yana da zafi a yau, gobe ne amma dole ne mu baiwa magoya bayanmu kwazon da suka dace a mako mai zuwa.”
A wani labarin kuma, Ganduje Ya Mayar Da Martani Kan Sautin Hirar Su Dake Yawo A Kafofin Sada Zumunta
Gwamnatin jihar Kano ta yi gargadi da babbar murya ga jama’ar Kano, game da yaɗa barna, yaudara, wuce gona da iri da suka tsiri yi a kwanan nan.
Gwamnatin jihar Kano ta bayyana hakan da masu aikata hakan a matsayin masu zagon kasa, kuma hakan tamkar wani yunkuri ne da kafafen sada zumunta suke son koya, ta hanyar yaɗa sautin tattaunawa ta wayar tarho tsakanin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da Ibrahim Kabiru Masari wadda ta shafi alakarsa ta siyasa da zababben shugaban kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
Kwamishinan Yada Labarai da kula da Harkokin Cikin Gida na Jihar, Malam Muhammad Garba a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, ya bayyana cewa fitar da sautin na matsayin wani yunkuri na wasu bata gari, wadanda ke da manufar tayar da zaune tsaye.