Hukumar Hisba dake jihar Kano ta kama aƙalla mabarata 648 dake yawon bara akan titunan jihar tun daga watan Fabrairu zuwa yanzu.
Mai magana da yawun hukumar, Lawan Ibrahim, ya ce waɗanda aka kama ɗin an kama su ne a titunan Bata da Murtala Muhmamed da Asibitin Nasarawa da hanyar jirgin ƙasa da kuma Titi gwamnatin jiha a cikin garin Kano. Mata 416 ne da kuma maza 232 aka kama.
Ibrahim ya ce hukumar za ta ci gaba da kama masu bara da suka ki bin dokar hana bara da gwamnatin ta saka.
“Za mu tabbatar da hana bara a titunan Kano.
“An kuma tantance waɗanda aka kama, haka kuma wanda aka samu laifinsu ne na farko za a miƙa su wajen ‘yan uwansu.
“Waɗanda kuma suka saba yi za mu kai su kotu domin a yanke musu hukunci.”
Idan ba a manta ba a watannin baya gwamnatocin arewa sun hana yin bara a jihohin arewar ciki har da jihar Kano idan gwamnan jihar Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya tabbatar da dokar hana barar.