‘Yan Najeriya da dama na ta maida martani a shafuka da zaurukan sada zumunta, akan auren ‘yar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, Hanan da aka yi a makon da ya gabata.
Ma’abota ziyartar shafukan sada zumunta sun ci gaba da sukar shugaba Buhari da ma gwamantinsa dangane da nuna halin ko in kula da ‘yan Najeriya ke ci.
Wasu kuma sun yi ta sukarsu sakamakon yin biki a lokacin da aka gindaya dokoki waɗanda suka haramta cunkoson jama’a.
Sai dai a wani ɓangare matar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, wato Aisha Buhari ta maida martanin cewa bikin ba kowa aka gayyata ba saboda bin dokar bada tazara da hana cunkoso.
Bikin auren Hanan Muhammadu Buhari da angonta Muhammad Turab Sha’abab, ya zo ne a dai-dai lokacin da ‘yan Najeriya ke ƙorafin hauhawa da kuma ƙarin farashin kayakin masarufi, man fetir da kuma ƙari a kuɗin wutar lantarki da aka yi.
Ɗan fafutuka kuma shugaban ƙungiyar CODE, dake rajin bin diddigin kuɗaɗen da aka yi sama da faɗi da su, Hamzat Lawal ya ce bai kamata iyalan farko a Najeriya ƙarƙashin shugaba Muhammadu Buhari su yi irin wannan biki a cikin yanayi da ƙasar nan ke fama da annobar Korona ba.
Mai zanen barkwancin nan Mustapha Bulama, shi ma ya yi zane inda ya nuna halin da ‘yan Najeriya ke ciki na wuya amma shugaban ƙasa ya aurar da ɗiyar tasa, wanda daga bisani matar shugaba Buhari, Aisha ta bayyana rashin jin daɗinta game da zanen da aka yi.