By Abbas Yakubu Yaura
Rundunar tsaron farin kaya ta Najeriya, NSCDC, reshen jihar Osun, ta cafke wasu mutane uku da ake zargi da safarar gurbataccen man fetur.
Kwamandan NSCDC a jihar, Emmanuel Ocheja, ya gabatar da wadanda ake zargin; Adeyeye Emmauel, Nasiru Adamu da Isa Mohammed a hedkwatar hukumar da ke Osogbo, babban birnin jihar.
Ocheja ya ce, an kama mutanen uku ne a mahadar Ibodi, Ilesa, dauke da jarkoki 19 na gurbataccen mai na lita 25.
Sai dai wadanda ake zargin sun musanta zargin.
Ocheja ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu domin ya zama darasi ga wasu.