A jiya Laraba ne majalisar dokokin jihar Edo ta kulle majalisar tare da komawa tsohon dakin taronsu dake cikin fadar gwamnatin jihar.
Hakan ya fito ne daga wata takarda da kakakin majalisar Yahaya Omogbai, ya fitar ga manema labarai.
Ya ce “biyo bayan feshi da gyaran kujeru, da wutar lantarki da sauran gyararraki da za a yiwa majalisar a yanzu haka mun koma zamanmu cikin tsohuwar majalisa dake fadar gwamnati”.
Shugabancin majalisar ya amince da dawowa da ci gaba da zama a majalisar a ranar 29 Yuni 2020 da misalin karfe 10 na safe.
Ya kara da cewa “dukkaknin masu ruwa da tsakin majalisar da kuma mutanen gari ana sanar da su sabon canjin da aka samu kuma za a ci gaba da zama a can har zuwa lokacin da za a kammala gyare-gyaren”.