By Abbas Yakubu Yaura
Wata kungiyar kare hakkin bil’adama da ci gaban jama’a a cibiyar kare hakkin jama’a da ci gaban kasa reshen jihar Kwara, ta soki matakin da majalisar dokokin jihar ta dauka kan nadin Hajiya Halimat Kperogi a matsayin magatakardar majalissa na tsawon shekara guda.
Idan dai ba a manta ba Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa majalisar dokokin jihar a zamanta na ranar 30 ga watan Maris, 2022, ta tabbatar da nadin Hajiya Jummai Halimat Kperogi mai ritayar kan kwangilar shekara daya a matsayin ma’aikaciyar majalisar.
Najeriya Zata Kara Haraji A Kan Taba Sigari Da Shisha Da Sauran Su A Ranar 1 Ga Watan Yuni
A cikin wata sanarwa da babban daraktan kungiyar kuma shugaban hukumar kula da rikice-rikice na kungiyar Barista Luqman Shaffii da Barista L. A. Oladimeji suka fitar, kungiyar ta ce shugaban majalisar ne ya sanya takarar Hajiya Kperogi a kan ‘yan majalisar. Kungiyar wacce ta ce tun da farko an amince da nadin ma’aikaciyar a kan kwangilar na tsawon watanni shida wanda ya kare a ranar 29 ga watan Maris, ta bayyana cewa.
“Cibiyar ba ta da masaniya kan kudurin da Majalisar Dokokin Jihar Kwara ta yi a zamanta na ranar 30 ga watan Maris, 2022, inda tace ba bisa ka’ida ba ta tabbatar da nadin wata Hajiya Jummai Halimat Kperogi kan kwangilar shekara guda a matsayin magatakardar majalisar dokokin jihar.
“Mun san cewa tun da farko an amince da nadin kwangilar na tsawon watanni shida.
“A rubuce yake cewa mai girma kakakin majalisar ne ya dorawa ‘yan majalisar takarar Hajiya Jummai Halimat Kperogi. Muna so mu bayyana sarai cewa duka na farko da na yanzu na tabbatar da nadin kwangilar ba bisa ka’ida yake ba.
“Tsarin dokar hukumar yi wa Majalisar Dokokin Jihar Kwara ta shekarar 2018, kamar yadda aka yi wa kwaskwarima ba ta da wata ma’ana kamar yadda za a iya samu a sashe na 9 na dokar cewa darakta a mataki na 17 ne kadai za a iya nadawa a matsayin magatakarda na majalisar, kuma babu wani ma’aikacin majalisar wakilai ma’aikatan kwangila ko wanda ya yi ritaya bai dace da nadin ba.
“A halin da ake ciki, muna so mu shawarci Mai girma shugaban majalissar da:Hajia Jummai Halimat Kperogi da aka nada a matsayin magatakardar majalisar ba bisa ka’ida ba tare da rokon ta da ta ci gaba da yi mata ritaya cikin gaggawa kamar yadda dokar ma’aikatan gwamnati ta tanada.
“Ku gabatar da zama, ku yanke shawarar nada duk wani jami’in da ya cancanta a matakin 17 a cikin Hukumar.
Idan babu wani jami’in da ya cancanta ko kuma wanda bai dace ba a cikin majalisar, majalisar za ta iya neman canji ko nazartar ma’aikatan da suka cancanta a kowanne ofishin gwamnati.
“Don haka muna ba (Majalisar Dokokin Jihar Kwara) shawar da ta tuntubi ma’aikatar shari’a ta jiha domin samun shawarwarin da suka dace a kan shari’a.
“CIRDEV ta shawarci Majalisar Dokoki da ta yi abin da ake bukata cikin gaggawa saboda Cibiyar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakin da ya dace na doka kan lamarin.”
Comments 1