Kungiyar Masu taimaka wa ‘yan majalisar dokokin tarayya kan kafafen yada labarai na jam’iyyar APC sun bayyana goyon bayansu ga Sanata Mohammed Sani Musa na jihar Neja da ya zama shugaban jam’iyyar na kasa.
Mataimakan, a karkashin kungiyar National Assembly Progressive Media Aides, (NAPMAIDEs), a wani taron manema labarai da suka gudanar a Abuja, sun ce sun kuduri aniyar karfafa alaka a tsakanin ‘yan majalisar masu ci.
Shugaban kungiyar NAPMAIDEs, Prince Oyelude Oladele, ya ce amincewa da Sanatan na daga cikin ayyukan da suke yi na inganta da kuma goyon bayan muradun shugabanninsu na ciki da wajen majalisar tarayya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Rahama Hassan Matar Bawa Mai Kada tayi auren bazata
“Shi (Musa) kwararre ne mai dabara, mashahurin mai wayar da kan jama’a, kuma fitaccen jagora na maza masu yaki da nuna bambancin jinsi. Ba shi da wata zargin Madakalar ta cin hanci da rashawa, ko a kowace kotu ko kuma a hukumar yaki da cin hanci da rashawa,” inji shi.