A yan baya-bayan nan ne dai gwamnatin jihar Kano ta bada umarnin sauya wa wasu ma’aikatan jihar kimanin 5000 gurin aiki zuwa bangaren koyarwa.
Wannan mataki na sauya wa Wadannan ma’aikata guraben aiki dai kamar yadda gwamnatin ta ce, na zuwa ne duba da kwarewa da suke da ita a bangaren na ilmi.
Gwamnatin ta ce ta yi hakan ne da zummar rage karancin malamai da ake da shi a jihar, lamarin dake kawo tafiyar hawainiya wa Kudirin gwamnatin na bada ilmi kyauta a Jihar.
Kwamishinan Yaɗa labaran Jihar Muhammad Garba, ya ce ma’aikata da wannan sauyi ya shafa wadanda an zakulo su ne daga Sassan gwamnati da ma’aikatu da hukumomi, dukkannin su nada shaidar koyarwa don haka tilas ne a tura su makarantu ciki harda na gaba da sakandare don bada tasu gudunmawa.
Bisa kididdiga da aka yi a cewar Kwamishinan, akwai ma’aikata 575 da suke aiki a ma’aikatu, sassa da kuma Hukumomin gwamnati, yayin da ya ce ma’aikata 3, 712 dake aiki a kananan hukumomi 44 suna aiki ne fiye da guda.
Ya kara da cewa daga cikin wadannan adadi, 19 na da shaidar digirin digir-gir, sai 55 dake da digiri na biyu, 1,100 na da digirin farko kan harkar ilmi, yayinda 2, 366 nada shaidar koyarwa ta NCE inda kuma sauran 10 suke da Diploma a kan harkar ilmi.
Jihar Kano wacce ita ce Jiha mafi yawan jama’a a faɗin arewa kana ta biyu bayan Jihar Legas a faɗin ƙasar nan, ta kasance ta gaba-gaba a Jihohin da yara ke karakaina Kororo-kororo ba tare da zuwa makaranta ba, inda ko da ilmin Firamare da ya zama kyauta kuma wajibi ba sa iya samu.