Masana harkokin kimiya sun ce yawon motsa jiki ka iya sanya lakar dan Adam da kuma Ƙwaƙwalwarsa daina aiki yadda ya kamata.
Sai dai masanan sun ce wannan na faruwa ne kawai ga wadanda garkuwar jikinsu ke iya samun matsalar.
Duk da wannan bincike da aka gudanar a Jami’ar Sheffield ta Birtaniya, amma masanan sun shawarci jama’a da cewa ba wai kuma suna nufin binciken nasu ya sanyaya gwiwa ba ne, don haka kowa ya ci gaba da motsa jikinsa.
https://www.sciencedirect.com/science/article/pii/S2352396421001900
Sa dai sun ce suna fata wannan bincike nasu zai bude kofa ga jama’a da a rika gwadasu don tabbatar da cewa suna da hatsarin shiga wannan matsala.
Binciken nasu ya gano cewa ko wane mutum guda cikin 300 ka iya fuskantar hatsarin kamuwa da cutar kwakwalwa da ta laka.
https://www.bbc.com/news/health-57431412
Sun ce hakan kazalika na iya sanya dan Adam kasa motsawa ko magana ko uwa uba ma numfashi, domin jijiyoyi dake aika sako daga Ƙwaƙwalwa zuwa ga gabobi sun kasa aiki.
Yanzu haka masanan sun ce wannan al’amari ka iya rage tsawon rayuwa dan adam.