Majalisar tarayya ta shiga tsakani lamarin rikicin harajin da ya ɓarke tsakanin hukumomin tara kuɗaɗen shiga na tarayya.
Rikicin ya kunno kai ne bayan hukumar tara kuɗaɗen shiga ta ƙasa (FIRS) ta zargi hukumar gidan waya ta ƙasa (NIPOST) da buɗe asusun ajiyar kuɗaɗen ba bisa ka’ida ba.
“A matsayin kwamitin lura da hukumomin kuɗi, mun kira ku ne mu gani ko kuna bin doka”, inji Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai, James Faleke.
A zaman tattaunawan kwamitin da hukumomin kan kuɗin shiga biliyan 58, Faleke ya ce surutan da hukumomin ke yi babban abun kunya ne.
Zaman ya samu halarcin shugaban NIPOST, Ismail Adebanjo da Shugabar Kwamitin Amintattun hukumar Maimuna Yahaya Abubakar da wasu manyan jami’ai.
Yayin jawabi a kan kan kuɗin biliyan 58 na harajin da aka tara daga watan Fabrairun 2016 zuwa Afrilun 2020, shugaban FIRS Muhammad Nami ya ce sun tara naira biliyan uku na harajin kan sarki a duk sati daga bankuna kasuwanci.
Rikicin harajin kan sarkin ya taso ne a ‘yan makonnin nan bayan hukumomin sun fara cacar baki kan wane ne a cikinsu ke da hakkin tarawa.
FIRS ta zargi NIPOST da buɗe asusun ajiyar harajin a babban bankin Najeriya (CBN) ba bisa ƙa’ida ba, da yunƙurin facaka da kuɗaɗen.
NIPOST ta karyata zargin ta kuma ce ba ta da ikon taɓa kuɗaɗen.