Mataimakin gwamnan Jihar Neja Yakubu Garba ya shaida cewa kimanin mutane 6000 ne suka tsere daga muhallinsu sakamakon iftala’in ambaliya ruwa da kuma ayyukan yan fashin daji.
Mataimakin Gwamnan ya shaida hakan ne a yayin wata ziyara da ya kaiwa shugaban Hukumar bada agajin gaggawa ta ƙasa NEMA a birnin Tarayya Abuja.
KARANTA WANNAN LABARIN: Shugaba Bola Tinubu ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi hakuri da gwamnatinsa dangane da cire tallafin man fetur, yana mai cewa matakin na da amfani ga kasar.
Wannan ziyara ta Mataimakin gwamnan na zuwa ne yayin yan fashin daji ke ci gaba cin karensu babu babbaka a wasu yankuna na jihar, a don haka ne ma ya miƙa buƙatar da a kai musu ɗoki.
Ya ƙara da cewa ambaliyar ruwa tana ci gaba da ɗaiɗaita Jihar don haka akwai buƙatar Hukumar NEMA ta shigo lamarin don samo bakin zarensa.
Ya ce “Jihar Neja tana fama da matsalolin tsaro daban daban wanda babu inda za mu kai kukanmu da ya wuce nan a halin da ake ciki”
“Ba’ada Zalika, hasashen yanayi ya nuna cewa akwai yiwuwar ta’azzarar ambaliyar ruwa a daminar bana wanda da ma mu mun daɗe fuskantar hakan a Jihar Neja”
Yakubu Garba bugu da ƙari ya ce a ɓangaren gwamnatin Jihar tana iya ƙoƙarinta domin tuni ake ci gaba da wayar da kan al’umma da su gagauta tashi daga inda iftala’in ya fi aukuwa don gudun aikin da-na-sani.
Da yake maida jawabi shugaban Hukumar NEMA ya ce hukumar kullum cikin ɗamara take na ganin ta baiwa dukkannin agaji ga waɗanda iftala’i ya shafa a fadin kasarnan.