- An amince da tsagaita wuta na wucin gadi a Sudan a fadan daya kaure tsakanin bangarorin da ke gaba da juna.
- Amma sabuwar yarjejeniyar za ta kasance ta “hanyar sa ido kan tsagaita bude wuta,”
- An bukaci dukkan sojojin gwamnati da na RSF da su ba da damar rarraba kayan agaji, maido da muhimman ayyuka da kuma janye sojoji daga asibitoci.
An amince da tsagaita wuta na wucin gadi a Sudan yayin da fada tsakanin bangarorin da ke gaba da juna ya shiga mako na shida, in ji BBC.
Yunkurin sasantawa da aka yi a baya tsakanin sojojin Sudan na yau da kullun da dakarun sa kai na RSF ya yi sanadiyar durkushewa lamura cikin ‘yan mintoci da farawa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Sudan: Bangarorin Da Ke Gaba Da Juna Sun Amince Da Tsagaita Bude Wuta
Amma sabuwar yarjejeniyar za ta kasance ta “hanyar sa ido kan tsagaita bude wuta,” a cewar sanarwar Amurka da Saudiyya.
A wani bangare na tsagaita bude wuta na jin kai na kwanaki bakwai, jami’an Sudan sun amince da dawo da muhimman ayyuka.
Fadan da ake gwabzawa tsakanin bangarorin biyu dai ya jefa kasar cikin rudani tun a watan da ya gabata, inda ake tunanin sama da mutane miliyan guda sun rasa matsugunansu.
Hannun jarin abinci da kudi da kayan masarufi sun ragu cikin sauri sannan kungiyoyin agaji sun sha yin korafin rashin samar da isassun taimako a birnin Khartoum na kasar Sudan, inda akasarin tashe tashen hankula yafi karfi.
An bukaci dukkan sojojin na yau da kullun da na RSF da su ba da damar rarraba kayan agaji, maido da muhimman ayyuka da kuma janye sojoji daga asibitoci.
Amurka da Saudiyya wadanda suka dauki nauyin tattaunawar zaman lafiya a Jeddah sun ce tsagaita wutar za ta fara aiki a yammacin ranar Litinin.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fitar ta amince da yunkurin wanzar da zaman lafiya a Sudan a baya wanda bai samu nasara ba, sai dai ta ce akwai babban bambamci a wannan karon.
“Ba kamar yadda aka cimma a baya ba, yarjejeniyar da aka cimma a Jeddah, bangarorin biyu ne suka rattaba hannu kan yarjejeniyar, kuma za ta samu goyon bayan Amurka da Saudiyya da kuma tsarin sa ido kan tsagaita bude wuta da kasashen duniya ke marawa baya, ba tare da yin karin bayani ba.
A yayin da yake magana a shafinsa na Twitter, sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya kara da cewa, “Lokaci ya wuce da za a rufe bakin bindiga tare da ba da damar kai agajin jin kai ba tare da wata tangarda ba.
“Ina kira ga bangarorin biyu da su kiyaye wannan yarjejeniya – idanun duniya suna kallo.”
JARIDAR DIMOKURADIYYA ta rawato cewa yakin ya barke a birnin Khartoum a ranar 15 ga watan Afrilu biyo bayan zaman dar dar da aka kwashe kwanaki ana yi yayin da aka sake tura mambobin kungiyar RSF a fadin kasar a wani mataki da sojojin ke ganin barazana ce.
A wani labarin kuma, APC Ta Dakatar Da Daukacin Jiga-Jigan Jam’iyyar Na Wata Karamar Hukuma
Jam’iyyar APC reshen jihar Kogi ta dakatar da dukkan jami’an zartaswa na daukacin sassan karamar hukumar Igalamela/Odolu.
Jam’iyyar ta kuma zargi jami’an da aka dakatar da karkatar da kudaden jam’iyyar da nufin durkusar da ita a jihar.
APC tace nan take an kafa wani kwamitin rikon kwarya don gudanar da al’amuran jam’iyyar a kananan hukumomin da abin ya shafa.