Wasu masu zanga-zanga daga tsagin jam’iyyar PDP dake jihar Neja sun yi wa babban ofishin uwar jam’iyya na PDP dake Maitama a Abuja cikar tsinke, tare da bukatar sauke sakataren jam’iyyar na ƙasa Abdullahi Maibasira daga muƙaminsa.
Masu zanga-zangar sun zargi Maibasira da haɗa baki da gwamnatin APC mai ci domin kawo wa jam’iyyar naƙaso.
Ɗaya daga cikin masu zanga-zangar mai suna Yahuza Hussaini daga Minna yace sun fito zanga-zangar ne domin jawo hankalin masu ruwa da tsaki game da cin dunduniyar jam’iyyar da ake yi.
Hussaini yace “muna so mu jawo hankalin shugabaninmu domin ba zamu bari Maibasira da tsohon kakakin majalisar jihar Neja Tanko Bego su sayar da jam’iyyar PDP reshen jihar Neja ba”.
“Shugaba ɗaya kawai muka sani a jam’iyyar PDP shi ne Babangida Aliyu Talban Minna, saboda ko lokacin da aka rasa mulki ba inda yace har suka fita suka dawo yana nan”, cewar Hussaini.
Masu zanga-zangar sun bayyanawa jaridar Punch cewa basu bar ofishin uwar jam’iyyar ba har sai an karɓi ƙorafinsu tare da alƙawarin ɗaukar mataki.