• Yan bindiga sun yi garkuwa da wani basaken a jihar Ekiti lokacin dayake gona da matar shi.
• Sai da ya roki yan bindigan kafin suka amince sukyale matarshi, inda suka ta Fi da ita.
• Makamancin hakan ya taba faruwa, inda a kayi garkuwa da wani basaken watanni biyu dasu ka gabata.
Yan bindiga sun yi garkuwa da wani basaraken Gargajiya da yammacin jiya juma’a, a gonar shi, lokacin ya na tare matar shi, jihar Ekiti.
Wani rahoton ya bayyana cewa, yan bindigan sun kame basaken ne da matar shi lokacin da suka je gona.
KARANTA WANNAN LABARIN: Boko Haram batakai hari sansanin sojin sama na Kaduna ba
Sai dai a nan take, basaraken ya roki yan bindigan da su bar matar shi, su tafi da shi, inda kuma suka amince da bukatar ta shi.
A cewar rahoton Kwamandan rundunar tsaro ta Amotekun reshen jihar Ekiti Birgediya Komolafe ya tabbatar da afkuwar lamarin, inda ya ce, “Tuni jami’an yan sanda, na soji, na Amotekun da Tawagar Mafarauta da kuma wasu kungiyoyi sa Kai, sun bazama cikin dazukan, domin kubutar da basaraken a hannun yan bindigan”
Wannan lamari dai na zuwa ne biyo bayan afkuwar makamancin shi, a watanni biyu da su ka gabata, inda a kayi garkuwa da wani basaraken garin Ilemeso Ekiti, Mai suna Oba David Oyewumi a fadar shi, da ke yankin Oye
Comments 1