Gwamnan Jihar Borno Babagana Umara Zulum ya badar umarnin dakatar da ayyukan wata kungiyar kasa da kasa mai suna ACTED a jihar.
Wannan umarni na Zulum na zuwa ne bayan da aka samu Ƙungiyar da hannu dumu-dumu tana koyawa wasu matasa yadda ake amfani da bindiga a wani otal.
Kakakin Gwamna Zulum mai suna Isah Gusau wanda shine ya sanar da wannan mataki, ya ce an gano wannan mummunan aika-aika ne da kungiyar ke yi bayan da ta boye matasan a hotel dake hanyar Maiduguri tana musu harba bindigar da bindigar roba.
Gusau ya bayyana cewa an samu nasarar gano wannan lamari ne bayan da mazauna kusa da otal din suka kai wa jami’an yan sanda rahotan jin karar harbe-harbe.
Kazalika bayan garzayawa otal din ne, yan sanda suka samu bindiga kirar pistol da wasu mutane biyu yan Najeriya da sune ke koyawa matasan wannan mugun aiki.
Yanzu haka gwamna Zulum kuma ya bada umarnin rufe otal ɗin tare tare da haramta ayyukan kungiyar ta ACTED har sai abinda binciken yam sanda ya gano.