Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari zai tafi Jamhuriyar Nijar a yau Litinin domin halartar taron shugabannin ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) kan yaƙi da annobar Korona.
A watan Afrilu ƙungiyar ta ECOWAS ta naɗa shugaba Buhari a matsayin shugaban kwamitinta na yaƙi da cutar, wanda zai gabatar da rahoto a taron na yini guda.
Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Malam Garba Shehu, ya ce Buhari zai jagoranci yaƙar annobar cutar Korona a yammacin Afirka.
Zauren shugabannin ECOWA ya kuma zaɓi ministocin Najeriya na lafiya da sufurin jiragen sama da na kuɗi a matsayin shugabannin kwamitocin da suka shafi ma’aikatunsu, wanda Buhari zai jagoranta domin samun nasara a yaƙi da Koron.
Taron zai kuma karɓi rahoto a kan samar da takardar kuɗin bai-ɗaya na ECOWAS daga Julius Midara na ƙasar Saliyo da kwamitinsa.
Shugaban hukumar ECOWAS, Jean Claude Kassi Bou, zai gabatar wa taron rahoton wucin gadi a kan muradun ECOWAS na shekarar 2020 da sauransu.
Sauran batutuwan da taron zai tattauna sun haɗa da ƙaruwar matsalar tsaro a yankin da kuma rikicin siyasar kasar Mali.