…Jam’iyyar yan kwadago ta Labour LP ta kammala shirinta na kalubalantar sakamakon zaben gwamnan jihar da ta ce ita ce ta yi.
Jam’iyyar Labour LP, na shirin kalubalantar nasarar Gwamna Babajide Sanwo-Olu a zaben gwamnan Legas da aka yi ranar 18 ga watan Maris.
A ranar 20 ga watan Maris ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana Sanwo-Olu na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben kuma zababben gwamna.
Jaridar DIMOKURADIYYA ta tattaro cewa Wanda ya lashe zaben ya samu kuri’u 762,134, inda ya doke Gbadebo Rhodes-Vivour na jam’iyyar LP wanda ya samu kuri’u 312,329. Olajide Adediran na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 62,449.
KU KARANTA KUMA Babu Wasu Shaidu Na Gaske Da Zasu Tabbatar An Kaiwa Dan Takarar LP Hari
Sakamakon da jami’in da ke kula da zaben Farfesa Adenike Temifayo-Oladiji, mataimakin shugaban Jami’ar Fasaha ta Tarayya ta Akure ya sanar, ya nuna 1,182,620 da suka amince da kada kuri’a, kuri’u 1,173,631 da aka kada, sannan 17,953 suka ki amincewa da.su.
Wani Tashin hankali da aka rawaito gaban zaben ya kai ga a ranar zabe, magoya bayan jam’iyyar APC, suka hana ‘yan kabilar Igbo, da kuma ‘yan kabilar Yarbawa su yi.
Dubban mazauna jihar ba su iya kada kuri’a a sassa da dama a fadin jihar ba bayan cin zarafi, tsoratarwa, da tashin hankali da suka hada da amfani da muggan makamai.
Kafin sanarwar, Shugaban Jam’iyyar LP a Legas, Dayo Ekong ya koka kan yadda aka hana mutane kada kuri’a a Alimosho, Eti-Osa, Ibeju-Lekki, da sauran kananan hukumomi.
“Babu sakamakon sama da 1,000. Mutane sun mutu… an hana mutane hakkinsu. Wannan zaben shirme ne…zaben da aka yi tashe-tashen hankula!
“Ina so in gaya maka, Mista Gbaje, REC, cewa ka gaza yiwa matasa. Kun gazawa talakawa, kuma ba ku yi abin da ya dace ba,” in ji ta.
A cikin jawabinsa, Rhodes-Vivour, wanda aka fi sani da GRV, ya yi zargin cewa “haɗin kai” ne tsakanin jam’iyyar APC da jami’an zaɓe a ƙoƙarin dawo da Gwamna Sanwo-Olu.
“Sakamakon da INEC ta fitar ba ya wakiltar muradin mafi yawan ‘yan Legas masu zaman lafiya, sakamakon wakilanmu da yanayin da muke ciki ya nuna cewa mun yi nasara,” in ji shi.
Jaridar Daily Post ta rawaito cewa Yanzu haka dai dan takarar da jam’iyyarsa sun garzaya kotu, suna neman soke zaben INEC.
Daya daga cikin makusantan Rhodes-Vivour ya tabbatar da cewa ana shirin kammala shirye-shiryen shigar da kara a Kotun Zaben Gwamna.
A Wani Labarin Kuma Mun Saki Biliyoyin Naira Domin Bankuna Su Wadata Yan Kasa – CBN
Babban bankin Najeriya CBN ya ce kawo yanzu ya saki kudi masu yawan gaske ga Bankunan kasuwanci a kasar
A cewar bankin ya saki kudin ne ga Bankunan, domin su samu damar baiwa al’umma da suke tsananin bukatar kudin a hannu yanzu haka.