A kokarin sa na ganin jihar Kaduna ta Zama abar sahun gaba-gaba a Nageriya dama kasashen duniya Sanata malam Uba Sani ya jagoranci tawagar Yan jarida zuwa duba Ayyukan cibiyoyin wasanni a jihar ta Kaduna, Wanda yanzu haka ake Kan ginawa hakan na kunshe ne acikin wata sanarwa da Sanatan ya fitar Yana Mai cewa.
“A yau, na jagoranci wata tawaga mai karfin gaske wacce ta kunshi manyan jami’an gwamnatin jihar Kaduna, gami da yan jaridu, a ziyarar duba aikin ci gaba da gina cibiyoyin wasanni a matsayin wani ɓangare na Ayyuka da suka shafi shiyyata da nake wakilta. A cikin tawagar ta binciken Ayyukan akwai Kwamishinan Wasanni da matasa na Jihar Kaduna, Farfesa Kabir Mato, da mai ba Gwamna El-Rufai shawara kan harkokin yada labarai da sadarwa wato Mista Olumuyiwa Adekeye.” Inji Sanata Uba Shi.
“Kafin in fara wannan rangadi na yi jawabi ga Yan jarida tawagar taron manema labarai na hadin gwiwa tare da Farfesa Kabir Mato inda na wa ‘yan jarida Karin haske da dalilan da suka sa aka samu saukin kan gina cibiyoyin wasannin. Na sanar da su cewa za mu fara tare da kawo Cigaban Cibiyoyin Wasannin don samar da dama ga matasan mu don haɓaka hazaƙarsu su kasancewa cikin koshin lafiya da mu’amala ta hanyar da ke haifar da jin daɗin jama’a da haɓaka zaman lafiya. Domin Jihar Kaduna ta cigaba da kere sa’a a wasanni daban -daban. Tabbas Wasanni yana daya daga cikin manyan abubuwan dake samawa matasa aikinyi. Idan an yi amfani da shi yadda yakamata kuma an bunƙasa shi amatsayin wani sashin kasuwanci, ɓangaren wasanni yana da damar ba da gudumma wa ta musamman don yaƙi da talauci da rashin aikin yi ga matasa.” Inji shi.
“Wannan wani yunkuri ne domin Samar abubuwan more rayuwa na gwamnan mu mai ƙwazo tare da aiwatar da ƙwaƙƙwaran ayyukanmu, Malam Nasir El-Rufai. Har ila yau, duk wannan Yana cikin kokari tare da goyon da muka samu daga jama’armu da nake wakilta Wanda suka bani kuri’u Bayan cikakken goyon baya daga Gwamna malam Nasir El rufa’i Wanda yanzu haka sanadiyyar hakan Ina majalisar dattijan Nageriya” a cewar shi.
ya Kara da cewa, “Ba tare da cika gari da surutu ba, na kuma sanar da manema labarai maza da mata a taron na manema labarai da suka halarta cewa ina da alfarmar sauƙaƙe babban matakin da duk wani ɗan majalisar dokokin Najeriya a hukumomin jihar da Najeriya. Na sauƙaƙe ginin Injiniyanci na Naira Biliyan 3, na Jami’ar Jihar Kaduna, Wannan gagarumin aikin zai taimaka wajen magance karancin ma’aikata a jihar Kaduna.”
Kazalika Sanata Uba Sani ya ce, “Na kuma yi muhimman ayyuka a cikin kananan hukumomi 7 na shiyyar Kaduna ta tsakiya.wanda Suka hada da ginawa da samar da dakunan kwana Mai daukar gado dari da goma 110 a makarantun sakandare da bunƙasa fasahar kasuwanci da harkokin Noma da -kasuwancin noma gina rijiyoyin burtsatse/ girka fitilun da ke amfani da hasken rana, da ginawa da samar da cibiyoyin ICT a Makarantun Sakandare.”
Ana kuma ci gaba da yin ayyukan wasanni Kamar
(1) Cibiyar Wasanni a Narayi
(2) Cibiyar Wasanni a Kajuru
(3) Cibiyar Wasanni a Tudun Wada
(4) Cibiyar Wasanni a Rigasa
5) Cibiyar Wasanni a Kawo
Sanatan ya kara da cewa, ya yin da na yi alkawarin ci gaba da ƙaddamar tare da aiwatar da ayyukan da za su yi tasiri ga rayuwar mutanen kirkinmu na Kaduna ta Tsakiya dama jihar Kaduna gaba ɗaya, na yi kira ga masu ruwa da tsaki, musamman ‘yan kasuwa domin Jan hankali su zuwa ga Shiga shirin tsarin Cibiyoyin Wasannin. Domin cigaban Cibiyoyin Wasannin Kuma sun yi alƙawarin zama masu chanja tsarin wasan zuwa wani mataki a ƙoƙarin da muke yi na samar da hanyoyin da matasanmu za su gane abubuwan da suke a tare dasu masu mahimmanci da kuma yin aiki na gari. Inji Sanata Uba Sani