Mataimakin gwamnan jihar Kwara kuma shugaban kwamitin ƙwararru na yaƙi da cutar Korona a jihar, Kayode Alabi, ya warke bayan kamuwa da cutar.
Sanarwar da mai magana da yawun kwamitin, Rafiu Ajakaye, ya fitar a safiyar Asabar ta ce gwaje-gwajen ƙarshe da aka yi wa mataimakin gwamnan sun nuna babu ƙwayoyin cutar a jikinsa.
“Hakan ke nufin mataimakin gwamnan ya warke daga cutar kuma zai dawo bakin aikinsa”, inji shi.
Ya ce amma har yanzu iyalin mataimakin gwamnan na ɗauke da cutar kuma suna ci gaba da karɓar kulawa. “Gwamantin jihar na wa matar mataimakin gwamnan da sauran masu fama cutar addu’ar samun lafiya”.
Sanarwar ta ƙara da gode wa mutanen jihar bisa addu’o’i da goyon bayansu da kuma ma’aikatan lafiya bisa sadaukar da kansu a yaƙi da cutar.
Ta kuma buƙaci al’ummar jihar da su ci gaba da kula da matakan da ake bi domin ganin bayan cutar a faɗin Jihar.