Ƙananan hukumomi 18 a faɗin Najeriya ke fuskantar barazanar dokar kulle kasancewarsu ɗauke da kaso ma fi yawa na masu ɗauke da cutar ta Korona.
Shugaban Kwamitin yaƙi da cutar Korona na ƙasa Boss Mustapha, bayan gabatar wa Shugaba Buhari rahoton kwamitin a ranar Litinin 29 ga watam Yuni, ya nuna buƙatar dokar kulle a ƙananan hukumomim domin daƙile yaɗuwar cutar.
“Matakin kulle a ƙananan hukumomin 18 ba hurumin gwamnatin tarayya ba ne, hurumi ne na gwamnatocin jihohi da na ƙananan hukumomi”, kamar yadda ya bayyana.
Daga ciki jerin ƙananan hukumomin akwai Lagos mainland, Mushin, Eti-Osa, Alimosho, Kosofe, Ikeja, Oshodi/Isolo, Apapa, Amuwo Odofin, Lagos Island da kuma Surulere.
Ragowar kuma sun haɗa da Abuja Municipal, Tarauni (Kano), Nassarawa (Kano), Katsina, Maiduguri (Borno), Dutse (Jigawa), Oredo (Edo), Bauchi da kuma Ado Odo/Ota dake jihar (Ogun).