Wani mazaunin garin Port Harcourt, Kapav Riksha, ya ce ba zai amshi sadaki a hannun manemin auren diyarsa ba idan ta rasa budurcinta kafin aure.
Ya bayyana hakan ne a Facebook yayin da ya je mayar da martani ga wani mutum wanda ya je neman aure inda aka lissafo masa abubuwan da suka kusa N1.2m.
“Neman makudan kudade ga macen da ba budurwa ba damfara ce. Za ka iya wasu abubuwan al’adar amma ni dai ba zan amshi ko sadaki ba idan diyata ta rasa budurcinta kafin aure.”
Ya bayyana cewa:
“Ba wai ban san da batun fyade ba, a bangaren fyade kuma mijin ne zai bayyana abinda zai bayar. Babu wata bukata ta bayar da kudi mai yawa.”
Yadda amarya ta yafe wa ango sadakin aurenta tare da biya masa bashin N15.9m da ake bin sa
An samu labarin wata mata ‘yar kasar China wacce ta biya bashin yaun 180,000 wanda ya yi daidai da N15.9m da ake bin angonta bayan sun hadu da wata daya, Legit.ng ta ruwaito.
Bugu da karo kuma ta bayyana cewa ta yafe masa kudin sadakin da ya dace ya biya bayan haduwarsu da wata daya.
Yanzu haka sun yanke shawarar yin aure ranar 31 ga watan Disamban 2022. Ta kuma bayyana cewa ta yace masa zoben daurin aure da na sa rana. Masoyin nata mai suna Hu ya yi matukar nuna farincikinsa.